Skip to main content

YADDA AKE WANKAN GAWA

TUNATARWA

WANKAN GAWA DA YADDA AKE YINSA


FALALAR WANKAN GAWA

Al-Imam Hakim ya rawaito hadisi wanda Manzon Allah (s.a.w) yake cewa: ‘’Duk wanda ya wanke mamaci, kuma ya rufa masa asiri, Allah Zai gafarta masa sau arba’in.’’


A wani hadisin kuma Manzon Allah (s.a.w) Yace:

”Duk wanda ya wanke mamaci kuma yarufa masa asiri, to Allah zai tufatar dashi daga cikin tufafin Gidan Aljannah Kwarra, (wato Launin Tufafin).


SHARUDDAN WANKAN GAWA:

Daga cikin sharaddan wankan gawa sune:

{1}. Ana bukatar wadanda zasu wanke mamacin su zamanto makusantan sa misali: Iyaye. kanne ko yayyek “ya”yansa da sauransu).

{2}. Ana bukatar maza su jibinci wanke maza, suma mata su jibinci wanke mata (sai dai Miji zai iya wanke Matarsa haka ma Mace za ta iya wanke Mijinta).

{3}. Ba sharadi bane lallai sai anyi amfani da ruwan zafi.


YADDA AKE YIN WANKAN GAWA

Ana yin wankan gawa mara-mara ne misali:


    Sau Uku (3) ko
    Biyar(5) ko
    Bakwai(7) ko
    Tara(9).

Hakan ya tabbata daga Manzon Allah (s.a.w) a cikin hadisin Ummu Adiya (R.A).

Wadanda za su yiwa mamaci wanka su zasuyi la’akari suga wanka nawa yadace suyi masa.

Da farko dai kafin a fara wankan da akwai abubuwa guda Uku (3) da za’a fara yi wa mamacin.

Sune kamar haka:

{1}. Za’a cire masa suturar da take jikinsa, amma za’a sami dan kyalle a rufe masa al’aurarsa.

{2}. Bayan anyi abu na sama, sai kuma ayi masa tsarki, na bangaren mafuta biyu.
(Bawali da Gayadi).
{3}. Idan macece , za’a tsefe kitson da yake kanta, a wanke kan, sannan ayi Lallabi uku a kan ( wato Kalba guda Uku).
Sai a kwantar da Kalbar tayi bayan kan nata.Idan namiji mai kitso ne sai a warware kitson gaba daya.

YADDA AKE WANKA SAU UKU (3) Idan masu yiwa mamaci wanka sun zabi suyi masa wanka sau uku, to bayan sun gama abubuwan da suke sama saisu fara wankan. Da farko dai zasu tanadi ruwa kashi Uku (3), kowanne ruwa za'ayi wanka daya dashi. (RUWAN FARKO) Wannan wankan za'ayi wa mamacine wanka irin Wankan Janaba. Da farko za’a fara yiwa mamaci alwalane, kamar irin alwalar Sallah, sai dai wajen kuskurar baki da shakar hanci za’a shafa masa ruwane kawai a bakin da hancin. Bayan anyi masa alwala, sai kuma azuba ruwa a kansa a wanke masa har sau uku, sannan. kuma a wanke tsagin jikinsa na dama sannan na hagu. (RUWA NA BIYU) Bayan anyi masa wanka na sama wato na Janaba, sai kuma asami Sabulu ko Magarya ko Kanwa, a wanke mamacin dashi.
Wato za’a sami Soso da Sabulu a cuda jikinsa sosai (Kamar dai yadda ake wanka irin na Soso da Sabulu, saidai za’a iya amfani da Magarya ko Kanwa a maimakon Sabulun).
Bayan angama cuda shi sai a dauraye Kumfar da wannan ruwan. (RUWA NA UKU) Bayan anyi masa wanka na sama, wato na Soso da Sabulu, to sai kuma a sami ruwa na karshe wato na Uku a zuba Turare mai kamshi (Sosai) a ciki, sannan sai a wanke mamaci da shi.
Amfi son ayi amfani da Turaren Kafur, to amma idan ba’a same shiba to za’a iya amfani da duk wani Turare mai kamshi sosai. Bayan angama wankan Turaren, sai a tsane jikin mamacin asa masa Likkafani.

YADDA AKE YIN WANKA BIYAR (5), KO BAKWAI (7), KO TARA (9). Idan masu yi wa mamaci wanka sun zabi su yi masa wanka biyar (5), ko bakwai(7), ko tara(9). To wanka na biyu(2) wato na soso da sabulu shi za su yi ta maimaitawa. Amma dolene na Janaba shine a Farko, sannan na Turare shine a karshe.

MISALIN YADDA ZA AYI WANKAN SAU BIYAR (5).


{1}. Na farko shine na Janaba

{2}. Na biyu shine na soso da sabulu

{3}. Na uku shine na soso da sabulu

{4}. Na Hudu shine na Soso da Sabulu

{5}. Na Biyar shine na Turare.

YA UBANGIJI KASA MU CIKA DA IMANI AMIN.

Comments

Popular posts from this blog

KIMIYAR ALQUR'ANI DA ZAMANI A INA AKA HAƊU (1)

Kimiyyar Kur’ani Da Ta Zamani: A Ina Aka Hadu? (1) KIMIYYAR KUR'ANI DA ZAMANI By Baban Sadik Mun samu tambaya daga daya daga cikin masu karatu, wanda yake son sanin alakar dake tsakanin fahimtar malaman kimiyya na zamani kan abubuwan da suka shafi kimiyya, da kuma bayanin wasu abubuwa na kimiyya da Al-Kur’ani mai girma yayi. Shin, a ina suka hadu kuma a ina suka rabu? Wannan shi ne abin da zamu fara rubutu a kai daga wannan mako illa maa sha Allahu. A sha karatu lafiya. Tambaya “Abban Sadik, an ce masana Kimiyya na zamani sun tabbatar da wasu daga cikin Kimiyyar Al-Kur’ani mai girma. Wadanne ne daga ciki?” – Khaleel Nasir Kuriya, Kiru, Kano (GZG274): 07069191677 Gabatarwa Malam Khaleel Nasir muna godiya kwarai da wannan tambaya mai matukar muhimmanci, kuma Allah saka da alheri. Amsa wannan tambaya gaba dayanta na bukatar bincike na tsawon zamani mai dauke da hujjoji daga Kur’ani da kuma manyan littafan zamani. Domin harka ce da ta kumshi ilimi. Amma za mu yi iya kok...

UMMDATUL AHKAM: BABIN BAYANIN JININ HAILA

UMDATUL AHKAM باب الحيـــض: 40- عن عائشة رضي الله عنها "أَنَّ فَاطِمَةَ بِنْتَ أَبِي حُبَيْشٍ سألت النبي صلى الله عليه وسلم، فَقَالت: إِنِّي أُسْتَحَاضُ فَلاَ أَطْهُرُ، أَفَأَدَعُ الصَّلاَةَ؟ فقالَ: لاَ، إِنَّ ذَلِكَ دَمُ عِرْقٍ، وَلَكِنْ دَعِي الصَّلاَةَ قَدْرَ اْلأَيَّامِ الَّتِي كُنْتِ تَحِيضِينَ فِيهَا، ثُمَّ اغْتَسِلِي وَصَلَّى". وفي رواية: "وَلَيْسَتْ بِالْحَيْضَةِ، فَإِذَا أَقْبَلَتِ الْحَيْضَةُ فَاتْرُكِي الصَّلاَةَ فِيهَا، فَإِذَا ذَهَبَ قَدْرُهَا فَاغْسِلِي عَنْكِ الدَّمَ وَصَلِّي". BABUN DA ZAI YI BAYANI A GAME DA HUKUNCIN JININ HAILA: 40- An karvo daga (Nana) Aishatu (R.A) tace haqiqa Faximatu xiyar Abi Hubaishin ta tambayi annabin Allah (S.A.W.) sai tace (da shi): (Ya ma'aikin Allah) ni mace ce da nake yawan zubar jinin haila bani da tsarki shin ko na bar yin sallah? Sai ma'aiki (S.A.W.) yace da ita a'a, (ai ba kya bari ba) domin ai shi wannan wani jinin da yake zubowane daga wata jijiya (dake jikin mahaifa), sai dai ke abin da ya wajaba kiy...

Maganin Yawan Fitar Ruwa Mai Kai-kayj Afarjji

Ga Mata masu lalurar fitar ruwa masu Kaikayi daga Farjin su.  A gwada daya daga cikin wadannan:- 1)A samu Saiwar Garafuni da Sassaken Magarya, sai a tafasa, idan ya dan huce sai mace ta dinga kama ruwa da shi. Kullum sau daya. Yana maganin budewa da kaikayi. 2) A samu Garafuni da Sassaken Sanya sai a tafasa, mace ta dinga shan rabin kofi da safe, rabi da yamma. Yana fitar da dattin mara da maganin farin ruwa mai wari. . 3) A samu Furen Tumfafiya, sai a shanya ya bushe, a daka a dinga zubawa a cikin Nono ana sha. Yana magance matsalar ruwan infection. . 4) A samu Lalle da Ganyen Magarya da Kanumfari, a hada waje daya a daka sannan a tafasa a zuba farin miski a ciki. Idan ya dan huce sai ta shiga ciki ta zauna tsawon kamar minti goma. Yin haka yana maganin kaikayi da kuraje da budewa da dadewar gaba. 5) A samu Kabewa a dafa ta, bayan an dafa sai a tsame daga ruwa a jajjagata ko a birga, a zuba Madara ko Nono sannan a sa Zuma a sha. Wannan yana mganin rashin sha’awa da bushewa da rash...