UMDATUL AHKAM
باب الحيـــض:
40- عن عائشة رضي الله عنها "أَنَّ فَاطِمَةَ بِنْتَ أَبِي حُبَيْشٍ سألت النبي صلى الله عليه وسلم، فَقَالت: إِنِّي أُسْتَحَاضُ فَلاَ أَطْهُرُ، أَفَأَدَعُ الصَّلاَةَ؟ فقالَ: لاَ، إِنَّ ذَلِكَ دَمُ عِرْقٍ، وَلَكِنْ دَعِي الصَّلاَةَ قَدْرَ اْلأَيَّامِ الَّتِي كُنْتِ تَحِيضِينَ فِيهَا، ثُمَّ اغْتَسِلِي وَصَلَّى".
وفي رواية: "وَلَيْسَتْ بِالْحَيْضَةِ، فَإِذَا أَقْبَلَتِ الْحَيْضَةُ فَاتْرُكِي الصَّلاَةَ فِيهَا، فَإِذَا ذَهَبَ قَدْرُهَا فَاغْسِلِي عَنْكِ الدَّمَ وَصَلِّي".
BABUN DA ZAI YI BAYANI A GAME DA HUKUNCIN JININ HAILA:
40- An karvo daga (Nana) Aishatu (R.A) tace haqiqa Faximatu xiyar Abi Hubaishin ta tambayi annabin Allah (S.A.W.) sai tace (da shi): (Ya ma'aikin Allah) ni mace ce da nake yawan zubar jinin haila bani da tsarki shin ko na bar yin sallah? Sai ma'aiki (S.A.W.) yace da ita a'a, (ai ba kya bari ba) domin ai shi wannan wani jinin da yake zubowane daga wata jijiya (dake jikin mahaifa), sai dai ke abin da ya wajaba kiyi shine ki bar yin sallah gwargwadon kwanakin da kikeyin hailarki a ciki, sannan kuma sai ki yi wanka ki ci gaba da yin sallarki.
Amma a cikin wata ruwayar kuma cewa yayi (ai shi wannan jini ba jinin haila bane). Ke dai idan hailarki ta zo sai ki bar yin sallah a cikinta idan kuma gwargwadon yadda kike yin ta ya wuce sai kiyi wanka ki ci gaba da yin sallah.
41-وعن عائشة رضي الله عنها "أَنَّ أُمَّ حَبِيبَةَ اسْتُحَيْضَتْ سَبْعَ سِنِينَ، فَسَأَلَتْ رَسُولَ الله صلى الله عليه وسلم عَنْ ذَلِكَ؟ فَأَمَرَهَا أَنْ تَغْتَسِلَ، فَكَانَتْ تَغْتَسِلُ لِكُلِّ صَلاَةٍ".
41-An karvo daga Nana Aisha (R.A) tace Ummu Habibata ta kasance ta yi jinin istahala har na tsawon shekara bakwai (daganan) sai ta tambayi ma'aikin Allah (S.A.W.) akan haka? Sai shi kuma ya umarce ta da yin wanka sai ya zamo ta kasance tana yin wanka ga kowacce sallah (wato bata haxa sallah biyar da alwala xaya).
42-وعن عائشة رضي الله عنها قالت: "كُنْتُ أَغْتَسِلَ أَنَا ورسولُ الله صلى الله عليه وسلم مِنْ إِنَاءٍ وَاحِدٍ كَلاَنَا جُنُبٌ. وَكَانَ يَأْمُرُنِي فَأَتَّزِرُ، فَيُبَاشِرُنِي وَأَنَا حَائِضٌ.وَكَانَ يَخْرِجُ رَأْسَهُ إِلَيَّ وَهُوَ مُعْتَكِفٌ، فَأَغْسلُهُ وَأَنَا حَائِضٌ".
42-An karvo daga Nana Aishatu (R.A) tace ni na kasance ina yin wanka ni da ma'aikin Allah (S.A.W.) a cikin qwarya xaya, kowanne xayanmu yana da janaba, sannan ya kasance yana umartata sai in xaura zani shi kuma sai ya rungumeni alhali ina haila. Hakanan kuma ya kasance yakan turo min kansa a yayin da yake ittikafi (a masallaci) sai ni kuma in wanke masa alhali ina haila.
43-وعن عائشة رضي الله عنها قالت: "كان رسول الله صلى الله عليه وسلم يَتَّكِئُ فِي حِجْرِي وَأَنَا حَائِضٌ، فَيَقْرَأُ الْقُرْآنَ"
43-An karvo daga Nana Aishatu (R.A) tace manzon Allah (S.A.W.) ya kasance yana kashingixa akan cinyata alhali ina haila yakan kuma karanta alqur'ani yana kuma kashingixan akan cinyar tawa.
44- وعن مُعاذة قالت: "سألت عائشة رضي الله عنها فقلت: مَا بَالُ الْحَائِضِ تَقْضِي الصَوْمَ وَلاَ تَقْضِي الصَّلاَةَ؟ فقالت: أحَرُورِيَّةٌ أَنْتِ؟ فَقلت: لَسْتُ بِحَرُورِيَّة، وَلَكِنِّي أَسْأَلُ، فقالت كان يُصِيبُنَا ذَلِكِ، فَنُؤْمَرُ بِقَضَاءِ الصَّوْمِ وَلاَ تُؤْمَرُ بِقَضَاءِ الصَّلاَةِ".
44-An karvo daga Ma'azata (R.A) tace (wata rana) na tambayi (Nana) Asihatu (R.A) sai nace da ita wai shin mai yasa ne mai jinin haila zata rama azumi ba zata rama sallah ba? Sai kuwa Nana Aisha tace (da ita) au ko kema kina daga cikin masu aqidar Haruriyyanci ne? (wato Khawarijawa) sai ita kuma tace a'a, a'a, ko kaxan ni ba mai bin aqidar Haruriyyanci ba ce, sai dai kawai ni ina tambayane kawai (Daga nan sai ita Nana Aishar) tace mun kasance irin wannan xin yana samun mu sai kawai a umarcemu da mu rama Azumi amma ba'a umatarmu da rama sallah.
Comments
Post a Comment