Skip to main content

Posts

Showing posts from July 29, 2019

Ganduje Da Mataimakan Gwamnoni Uku Sun Tsalake Rijiya Da Baya

An tseratar da Ganduje da mataimakan gwamnoni 3 yayin da rikici ya kaure filin wasa a Kaduna legit.ng Jul 29, 2019 5:49 AM Gwamnan jahar Kano, Abdullahi Ganduje ya ga ta kansa yayin da rikici ya kaure a filin wasan kwallon kafa ta Ahmadu Bello dake garin Kaduna, ABS, inda har sai da Yansanda suka dinga harba barkonon tsohuwa a cikin jama’a. Rahoton kamfanin dillancin labarum Najeriya, NAN, ta bayyana cewa wannan lamari ya faru ne a ranar Lahadi, 28 ga watan Yuli bayan an kammala wasan karshe na gasar AITEO Cup tsakanin Kano Pillars da Niger Tornadoes. Majiyar Legit.ng ta ruwaito wasan ya kai ga bugun daga kai sai gola sakamakon kunnen doki da aka tashi, daga karshe Kano Pillars ta samu nasara da ci 4-3, sai dai magoya bayan Pillars sun shiga fili a guje don murna, inda jami’an tsaro suka taresu, daga nan fa sai rikici ya kaure, shine dalilin da yasa Yansanda suka shiga harba barkonon tsohuwa. Daga cikin wadanda rikicin ya rutsa dasu akwai gwamnan jahar Kano da ya je goy aba Pilla

Falalar Goma Farko Na Zul-Hajji

*Falalar Goman Farko Na Zul-Hajji* An karbo Hadisi Daga ibn Abbas (R.A) ya ce Annabi (SAW) ya ce: Ranar Daya Ga Watan zilhijja ita ce Ranar Da Allah (swt) ya Gafartawa Annabi Adam (A.S). Duk Wanda Ya Azimci Wannan Rana Allah(SWT) zai Gafarta Masa kowane irin zunubi tsakaninsa da shi. (2) Ranar biyu ga Zulhijja ita ce Ranar Da Allah (SWT) ya karbi Addu’ar Annabi Yunus (A.S) ya fitar da shi daga cikin kifin da ya hadiye shi. Wanda ya azimci wannan Rana yana da lada kwatankwacin wanda ya Raya shekara da ibada . (3) Ranar uku ga Zulhijja ita ce Ranar Da Allah (SWT) ya karbi Addu’ar Annabi Zakariyya (A.S) ya ba shi haihuwa. Duk wanda ya azimci wannan Rana Allah (SWT) zai karbi Adduo’insa. (4) Ranar Hudu Ga Zulhijja ita ce Ranar Da aka haifi Annabi Isah (A.S). Duk wanda ya Azimci wannan Rana Allah zai kare shi daga talauci da musibu. (5) Ranar Biyar Ga Zulhijja ita ce Ranar Da aka haifi Annabi Musa (A.S). Duk Wanda ya Azimci Wannan Rana Allah (SWT) zai kare shi daga munafunci ko azab