Skip to main content

ƘUNGIYAR MANOMA TAYI MAGANA

MANOMA: DAGA YANZU BUHUN SHINKAFA BA ZAIWUCE 15,000 BA.

By: Muhammadu Auwal Umar A korarin karfafa wa gwamnatin tarayya na hana fasakaurin shinkafa a kasar nan, kungiyar manoman shinkafa ta Nijeriya ta ce, daga yanzu buhun shinkafa ba zai wuce naira 15,000 ba. Da ya ke zantawa da manema labarai ranar Alhamin a garin Abuja, shugaban kungiyar manoman shinkafa na Nijeriya (RIPAN), Alhaji Mohammed Abubakar Maifata, ya bayyana cewa, kungiyarsa za ta hukunta duk wanda ta samu yana sayar da buhun shinkafa sama da farashin kungiya.
Ya kara da cewa, shinkafar gida da ake yi a Nijeriya ba ta wuce tsakanin naira 13,300 zuwa 14,000, yayin da ita kuma ta gwamnati ta kai 15,000. Kungiyar ta bayyana cewa, ta rubuta wa gwamnatin tarayya wasika wajen karya farashin shinkafa, domin ta karfafa wa gwamnati wajen hana fasakaurin shinkafa a kasar nan. Shuwagabannin kungiyar RIPAN sun bayyana cewa, Nijeriya tana asarar dala miliyan 400 wajen fasakaurin shinkafa daga kasar Jamhuriyar Benin.
Alhaji Mohammed Abubakar Maifata tare da matemakinsa Mista Paul Eluhaiwe sun bayyana cewa, sun kammala tuntubar mutanensu da ke bakin iyakar kasar nan. Shugaban kungiyar RIPAN ya ci gaba da cewa, akwai tan 500,000 na shinkafa da ake kan hanyar shigo da su kasar nan daga Thailand kafin bikin kirsimeti. A cewar shugaban kungiyar, ba shakka wannan zai sa masu fasakaurin shinkafa su yi asarar dala miliyan 4000. A bangaransa, rufe iyakar da ke tsakanin Nijeriya da kasar Benin zai taimaka wajen dakile fasakaurin shinkafa tare habbaka shinkafar gida.
Ya kara da cewa, kungiyar tana goyan bayan gwamnatin tarayya wajen kulle iyakar kasar nan. Kungiyar ta babbatar wa ‘yan Nijeriya cewa, za ta saka wa ‘ya’yan kungiyar haraji domin ta cike gurbin farashin shinkafa a kasuwa, sakamakon rufe iyakar kasar nan. Ta kara da cewa, kasar nan tana bukatar tan miliyan hudu na shinkafa a duk sheka, amma mambobin kungiyar za su shigo da shinkafa wanda ya kai tan miliyan biyar.
Mohammed Abubarkar ya ce, “tun daga watan Junairu har zuwa yau, ba a shigo da shinkafar da ta kai miliyan daya ba daga kasar Jumhuriyan Benin da Thailand da kuma India zuwa Nijeriya ta haramtacciyar hanya.
Ya kara da cewa, mafi yawancin shinkafar da ake shigowa da ita daga kasar Benin, ‘yan kasar Benin ba sa amfani da wannan shinkafa shi ya sa ake kawota Nijeriya. Lokacin da aka rufe iyakar kasar nan, ‘ya’yan kungiyar RIPAN sun bayyana cewa, “daga yau saun dauki damarar noman shinkafa yadda ya kamata.”
Mohammed Abubarkar ya ce, kungiyarsa sun kwashe sama da shekara biyu suna neman a rufe iyakar kasar nan, saboda su sauko da farashin shinkafa. A cikin bayanin da ya gabatar ranar Laraba a garin Abuja, mai magana da yawun shugaban kasa Mista Femi Adesina, ya bayyana cewa, shugaban kasa Buhari ya bayyana cewa, zai dauki mataki a kan masu safarar shinkafa lokacin da ya hadu da shugaban kasar Benin a kasar Japan. Shugaban kasar ya kara da cewa, ayyukan masu fasakaurin shinkafa yana kawo barazana ga tsarin da gwamnatinsa take yi wajen bunkasa harkokin noma.
A cewar shugaba Buhari, “a yanzu mutane suna komawa karkara domin su ci gaba da noma gonakinsu, kasar tana samun kudadan shiga, maimakon amfani da shinkafar kasar waje. Ba za mu taba barin yarda a ci gaban da fasakaurin kayayyakin ba,” in ji shi. Shugaban Nijeriya ya ce, mukasudin rufe iyakar kasar nan shi ne, ‘yan Nijeriya su bunkasa kayayyakin gida.
Tun da farko dai, shugaban kasar Benin Talon ya bayyana cewa, ya yi kira ga shugaban Nijeriya sakamakon alfanun da mutanen kasar suka samu game da rufe iyakar kasar.

Comments

Popular posts from this blog

KIMIYAR ALQUR'ANI DA ZAMANI A INA AKA HAƊU (1)

Kimiyyar Kur’ani Da Ta Zamani: A Ina Aka Hadu? (1) KIMIYYAR KUR'ANI DA ZAMANI By Baban Sadik Mun samu tambaya daga daya daga cikin masu karatu, wanda yake son sanin alakar dake tsakanin fahimtar malaman kimiyya na zamani kan abubuwan da suka shafi kimiyya, da kuma bayanin wasu abubuwa na kimiyya da Al-Kur’ani mai girma yayi. Shin, a ina suka hadu kuma a ina suka rabu? Wannan shi ne abin da zamu fara rubutu a kai daga wannan mako illa maa sha Allahu. A sha karatu lafiya. Tambaya “Abban Sadik, an ce masana Kimiyya na zamani sun tabbatar da wasu daga cikin Kimiyyar Al-Kur’ani mai girma. Wadanne ne daga ciki?” – Khaleel Nasir Kuriya, Kiru, Kano (GZG274): 07069191677 Gabatarwa Malam Khaleel Nasir muna godiya kwarai da wannan tambaya mai matukar muhimmanci, kuma Allah saka da alheri. Amsa wannan tambaya gaba dayanta na bukatar bincike na tsawon zamani mai dauke da hujjoji daga Kur’ani da kuma manyan littafan zamani. Domin harka ce da ta kumshi ilimi. Amma za mu yi iya kok...

UMMDATUL AHKAM: BABIN BAYANIN JININ HAILA

UMDATUL AHKAM باب الحيـــض: 40- عن عائشة رضي الله عنها "أَنَّ فَاطِمَةَ بِنْتَ أَبِي حُبَيْشٍ سألت النبي صلى الله عليه وسلم، فَقَالت: إِنِّي أُسْتَحَاضُ فَلاَ أَطْهُرُ، أَفَأَدَعُ الصَّلاَةَ؟ فقالَ: لاَ، إِنَّ ذَلِكَ دَمُ عِرْقٍ، وَلَكِنْ دَعِي الصَّلاَةَ قَدْرَ اْلأَيَّامِ الَّتِي كُنْتِ تَحِيضِينَ فِيهَا، ثُمَّ اغْتَسِلِي وَصَلَّى". وفي رواية: "وَلَيْسَتْ بِالْحَيْضَةِ، فَإِذَا أَقْبَلَتِ الْحَيْضَةُ فَاتْرُكِي الصَّلاَةَ فِيهَا، فَإِذَا ذَهَبَ قَدْرُهَا فَاغْسِلِي عَنْكِ الدَّمَ وَصَلِّي". BABUN DA ZAI YI BAYANI A GAME DA HUKUNCIN JININ HAILA: 40- An karvo daga (Nana) Aishatu (R.A) tace haqiqa Faximatu xiyar Abi Hubaishin ta tambayi annabin Allah (S.A.W.) sai tace (da shi): (Ya ma'aikin Allah) ni mace ce da nake yawan zubar jinin haila bani da tsarki shin ko na bar yin sallah? Sai ma'aiki (S.A.W.) yace da ita a'a, (ai ba kya bari ba) domin ai shi wannan wani jinin da yake zubowane daga wata jijiya (dake jikin mahaifa), sai dai ke abin da ya wajaba kiy...

Maganin Yawan Fitar Ruwa Mai Kai-kayj Afarjji

Ga Mata masu lalurar fitar ruwa masu Kaikayi daga Farjin su.  A gwada daya daga cikin wadannan:- 1)A samu Saiwar Garafuni da Sassaken Magarya, sai a tafasa, idan ya dan huce sai mace ta dinga kama ruwa da shi. Kullum sau daya. Yana maganin budewa da kaikayi. 2) A samu Garafuni da Sassaken Sanya sai a tafasa, mace ta dinga shan rabin kofi da safe, rabi da yamma. Yana fitar da dattin mara da maganin farin ruwa mai wari. . 3) A samu Furen Tumfafiya, sai a shanya ya bushe, a daka a dinga zubawa a cikin Nono ana sha. Yana magance matsalar ruwan infection. . 4) A samu Lalle da Ganyen Magarya da Kanumfari, a hada waje daya a daka sannan a tafasa a zuba farin miski a ciki. Idan ya dan huce sai ta shiga ciki ta zauna tsawon kamar minti goma. Yin haka yana maganin kaikayi da kuraje da budewa da dadewar gaba. 5) A samu Kabewa a dafa ta, bayan an dafa sai a tsame daga ruwa a jajjagata ko a birga, a zuba Madara ko Nono sannan a sa Zuma a sha. Wannan yana mganin rashin sha’awa da bushewa da rash...