Gwamnan jahar Kano, Abdullahi Ganduje ya ga ta kansa yayin da rikici ya kaure a filin wasan kwallon kafa ta Ahmadu Bello dake garin Kaduna, ABS, inda har sai da Yansanda suka dinga harba barkonon tsohuwa a cikin jama’a.
Rahoton kamfanin dillancin labarum Najeriya, NAN, ta bayyana cewa wannan lamari ya faru ne a ranar Lahadi, 28 ga watan Yuli bayan an kammala wasan karshe na gasar AITEO Cup tsakanin Kano Pillars da Niger Tornadoes.
Majiyar Legit.ng ta ruwaito wasan ya kai ga bugun daga kai sai gola sakamakon kunnen doki da aka tashi, daga karshe Kano Pillars ta samu nasara da ci 4-3, sai dai magoya bayan Pillars sun shiga fili a guje don murna, inda jami’an tsaro suka taresu, daga nan fa sai rikici ya kaure, shine dalilin da yasa Yansanda suka shiga harba barkonon tsohuwa.
Daga cikin wadanda rikicin ya rutsa dasu akwai gwamnan jahar Kano da ya je goy aba Pillars baya, akwai kuma mataimakan gwamnonin Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, na jahar Neja, Muhammad Ketso, da na Nassarawa, Eammnuel Akabe, kuma sauran manyan baki da dama.
Rikicin ya yi kamari ne bayan yan kato da gora sun shiga dukan magoya bayan Kano Pillars da gorori, inda suma magoya bayan Pillars suka sake shiri suka tunkari yan sa kai, aka yi ta fafatawa, da kyar Yansanda suka kori kowa daga cikin filin da barkonon tsohuwa.
Sai can bayan kura ta lafa shine shuwagabannin hukumar kwallon kafa ta Najeriya yi rabon lambobin yabo ga yan wasan da kungiyoyinsu, amma a lokacin kusan babu kowa a filin, ba kamar yadda ya yi cikar farin dango ba a yayin da ake doka wasan.
Comments
Post a Comment