Skip to main content

Falalar Goma Farko Na Zul-Hajji

*Falalar Goman Farko Na Zul-Hajji*

An karbo Hadisi Daga ibn Abbas (R.A) ya ce Annabi (SAW) ya ce:

Ranar Daya Ga Watan zilhijja ita ce Ranar Da Allah (swt) ya Gafartawa Annabi Adam (A.S). Duk Wanda Ya Azimci Wannan Rana Allah(SWT) zai Gafarta Masa kowane irin zunubi tsakaninsa da shi.

(2) Ranar biyu ga Zulhijja ita ce Ranar Da Allah (SWT) ya karbi Addu’ar Annabi Yunus (A.S) ya fitar da shi daga cikin kifin da ya hadiye shi. Wanda ya azimci wannan Rana yana da lada kwatankwacin wanda ya Raya shekara da ibada .

(3) Ranar uku ga Zulhijja ita ce Ranar Da Allah (SWT) ya karbi Addu’ar Annabi Zakariyya (A.S) ya ba shi haihuwa. Duk wanda ya azimci wannan Rana Allah (SWT) zai karbi Adduo’insa.

(4) Ranar Hudu Ga Zulhijja ita ce Ranar Da aka haifi Annabi Isah (A.S). Duk wanda ya Azimci wannan Rana Allah zai kare shi daga talauci da musibu.

(5) Ranar Biyar Ga Zulhijja ita ce Ranar Da aka haifi Annabi Musa (A.S). Duk Wanda ya Azimci Wannan Rana Allah (SWT) zai kare shi daga munafunci ko azabar kabari.

(6) Ranar shida ga Zilhijja ita ce Ranar Da Allah (SWT) ya yi Budin Alkhairi Ga Annabi (SAW). Duk Wanda ya Azimci Wannan Rana Allah zai dube shi da Rahama, kuma ba zai azabtar da shi ba.

(7) Ranar bakwai Ga Zulhijja ita ce Ranar Da Allah (SWT) zai sa a Rufe kofofin wuta, ba za a bude su ba har sai Wadannan kwanaki Goma sun wuce. Duk wanda ya Azimci Wannan Rana Allah zai Rufe masa kofofi talatin na tsanani a Rayuwarsa a buda masa kofofi talatin na sauki.

(8) Ranar Takwas Ga Zilhijja ita ce Ranar da ake cewa, Ranar tarayya. Duk wanda ya Azimci wannan Ranar, babu wanda ya san A Dadin Ladarsa sai Allah.

(9) Ranar tara ga Watan Zulhijja ita ce Ranar Hawan Arfa. Allah yana Gafartawa Duk Alhazan da ke wurin Arfa. Wanda kuma ba ya Wurin Aikin Hajji, idan ya Azimci Wannan Ranar, Allah yana Gafarta masa zunibinsa na shekarar Da ta Gabata, Da kuma shekarar Da ke tafe.

(10). Ranar Goma Ga Zulhijja ita ce Ranar layya. Duk wanda Allah ya horewa abin da zai yi layya, idan ya yanka Dabbarsa, Digon jini Na farko Da zai fara diga a kasa zai zama Gafara Gare shi Da iyalinsa.

An so Wanda zai yi layya Da wanda ba zai yi ba ya kame bakinsa sai bayan An Dawo Daga Sallah idi, ya ci abinci ko wani abu daga cikin layyarsa. Allah zai ba shi lada wacce ta fi Dutsen Uhud Girma Da Nauyi. Kuma ana so ya Raba Namansa kashi uku. Kashi Na farko Sadaka, kashi Na biyu kyauta, kashi Na uku kuma Domin iyali.

Allah Ya Bamu Ikon Azumtar Dukkan Wadannan Ranakun, kuma ya sadamu Da Falalar Da ya Tanadar Ga Masu Ibada A Wadannan Ranaku. Ameen Ya Allah.
✍Daga Dahiru Salihu*

Comments

Popular posts from this blog

KIMIYAR ALQUR'ANI DA ZAMANI A INA AKA HAƊU (1)

Kimiyyar Kur’ani Da Ta Zamani: A Ina Aka Hadu? (1) KIMIYYAR KUR'ANI DA ZAMANI By Baban Sadik Mun samu tambaya daga daya daga cikin masu karatu, wanda yake son sanin alakar dake tsakanin fahimtar malaman kimiyya na zamani kan abubuwan da suka shafi kimiyya, da kuma bayanin wasu abubuwa na kimiyya da Al-Kur’ani mai girma yayi. Shin, a ina suka hadu kuma a ina suka rabu? Wannan shi ne abin da zamu fara rubutu a kai daga wannan mako illa maa sha Allahu. A sha karatu lafiya. Tambaya “Abban Sadik, an ce masana Kimiyya na zamani sun tabbatar da wasu daga cikin Kimiyyar Al-Kur’ani mai girma. Wadanne ne daga ciki?” – Khaleel Nasir Kuriya, Kiru, Kano (GZG274): 07069191677 Gabatarwa Malam Khaleel Nasir muna godiya kwarai da wannan tambaya mai matukar muhimmanci, kuma Allah saka da alheri. Amsa wannan tambaya gaba dayanta na bukatar bincike na tsawon zamani mai dauke da hujjoji daga Kur’ani da kuma manyan littafan zamani. Domin harka ce da ta kumshi ilimi. Amma za mu yi iya kok...

UMMDATUL AHKAM: BABIN BAYANIN JININ HAILA

UMDATUL AHKAM باب الحيـــض: 40- عن عائشة رضي الله عنها "أَنَّ فَاطِمَةَ بِنْتَ أَبِي حُبَيْشٍ سألت النبي صلى الله عليه وسلم، فَقَالت: إِنِّي أُسْتَحَاضُ فَلاَ أَطْهُرُ، أَفَأَدَعُ الصَّلاَةَ؟ فقالَ: لاَ، إِنَّ ذَلِكَ دَمُ عِرْقٍ، وَلَكِنْ دَعِي الصَّلاَةَ قَدْرَ اْلأَيَّامِ الَّتِي كُنْتِ تَحِيضِينَ فِيهَا، ثُمَّ اغْتَسِلِي وَصَلَّى". وفي رواية: "وَلَيْسَتْ بِالْحَيْضَةِ، فَإِذَا أَقْبَلَتِ الْحَيْضَةُ فَاتْرُكِي الصَّلاَةَ فِيهَا، فَإِذَا ذَهَبَ قَدْرُهَا فَاغْسِلِي عَنْكِ الدَّمَ وَصَلِّي". BABUN DA ZAI YI BAYANI A GAME DA HUKUNCIN JININ HAILA: 40- An karvo daga (Nana) Aishatu (R.A) tace haqiqa Faximatu xiyar Abi Hubaishin ta tambayi annabin Allah (S.A.W.) sai tace (da shi): (Ya ma'aikin Allah) ni mace ce da nake yawan zubar jinin haila bani da tsarki shin ko na bar yin sallah? Sai ma'aiki (S.A.W.) yace da ita a'a, (ai ba kya bari ba) domin ai shi wannan wani jinin da yake zubowane daga wata jijiya (dake jikin mahaifa), sai dai ke abin da ya wajaba kiy...

Maganin Yawan Fitar Ruwa Mai Kai-kayj Afarjji

Ga Mata masu lalurar fitar ruwa masu Kaikayi daga Farjin su.  A gwada daya daga cikin wadannan:- 1)A samu Saiwar Garafuni da Sassaken Magarya, sai a tafasa, idan ya dan huce sai mace ta dinga kama ruwa da shi. Kullum sau daya. Yana maganin budewa da kaikayi. 2) A samu Garafuni da Sassaken Sanya sai a tafasa, mace ta dinga shan rabin kofi da safe, rabi da yamma. Yana fitar da dattin mara da maganin farin ruwa mai wari. . 3) A samu Furen Tumfafiya, sai a shanya ya bushe, a daka a dinga zubawa a cikin Nono ana sha. Yana magance matsalar ruwan infection. . 4) A samu Lalle da Ganyen Magarya da Kanumfari, a hada waje daya a daka sannan a tafasa a zuba farin miski a ciki. Idan ya dan huce sai ta shiga ciki ta zauna tsawon kamar minti goma. Yin haka yana maganin kaikayi da kuraje da budewa da dadewar gaba. 5) A samu Kabewa a dafa ta, bayan an dafa sai a tsame daga ruwa a jajjagata ko a birga, a zuba Madara ko Nono sannan a sa Zuma a sha. Wannan yana mganin rashin sha’awa da bushewa da rash...