Skip to main content

Falalar Goma Farko Na Zul-Hajji

*Falalar Goman Farko Na Zul-Hajji*

An karbo Hadisi Daga ibn Abbas (R.A) ya ce Annabi (SAW) ya ce:

Ranar Daya Ga Watan zilhijja ita ce Ranar Da Allah (swt) ya Gafartawa Annabi Adam (A.S). Duk Wanda Ya Azimci Wannan Rana Allah(SWT) zai Gafarta Masa kowane irin zunubi tsakaninsa da shi.

(2) Ranar biyu ga Zulhijja ita ce Ranar Da Allah (SWT) ya karbi Addu’ar Annabi Yunus (A.S) ya fitar da shi daga cikin kifin da ya hadiye shi. Wanda ya azimci wannan Rana yana da lada kwatankwacin wanda ya Raya shekara da ibada .

(3) Ranar uku ga Zulhijja ita ce Ranar Da Allah (SWT) ya karbi Addu’ar Annabi Zakariyya (A.S) ya ba shi haihuwa. Duk wanda ya azimci wannan Rana Allah (SWT) zai karbi Adduo’insa.

(4) Ranar Hudu Ga Zulhijja ita ce Ranar Da aka haifi Annabi Isah (A.S). Duk wanda ya Azimci wannan Rana Allah zai kare shi daga talauci da musibu.

(5) Ranar Biyar Ga Zulhijja ita ce Ranar Da aka haifi Annabi Musa (A.S). Duk Wanda ya Azimci Wannan Rana Allah (SWT) zai kare shi daga munafunci ko azabar kabari.

(6) Ranar shida ga Zilhijja ita ce Ranar Da Allah (SWT) ya yi Budin Alkhairi Ga Annabi (SAW). Duk Wanda ya Azimci Wannan Rana Allah zai dube shi da Rahama, kuma ba zai azabtar da shi ba.

(7) Ranar bakwai Ga Zulhijja ita ce Ranar Da Allah (SWT) zai sa a Rufe kofofin wuta, ba za a bude su ba har sai Wadannan kwanaki Goma sun wuce. Duk wanda ya Azimci Wannan Rana Allah zai Rufe masa kofofi talatin na tsanani a Rayuwarsa a buda masa kofofi talatin na sauki.

(8) Ranar Takwas Ga Zilhijja ita ce Ranar da ake cewa, Ranar tarayya. Duk wanda ya Azimci wannan Ranar, babu wanda ya san A Dadin Ladarsa sai Allah.

(9) Ranar tara ga Watan Zulhijja ita ce Ranar Hawan Arfa. Allah yana Gafartawa Duk Alhazan da ke wurin Arfa. Wanda kuma ba ya Wurin Aikin Hajji, idan ya Azimci Wannan Ranar, Allah yana Gafarta masa zunibinsa na shekarar Da ta Gabata, Da kuma shekarar Da ke tafe.

(10). Ranar Goma Ga Zulhijja ita ce Ranar layya. Duk wanda Allah ya horewa abin da zai yi layya, idan ya yanka Dabbarsa, Digon jini Na farko Da zai fara diga a kasa zai zama Gafara Gare shi Da iyalinsa.

An so Wanda zai yi layya Da wanda ba zai yi ba ya kame bakinsa sai bayan An Dawo Daga Sallah idi, ya ci abinci ko wani abu daga cikin layyarsa. Allah zai ba shi lada wacce ta fi Dutsen Uhud Girma Da Nauyi. Kuma ana so ya Raba Namansa kashi uku. Kashi Na farko Sadaka, kashi Na biyu kyauta, kashi Na uku kuma Domin iyali.

Allah Ya Bamu Ikon Azumtar Dukkan Wadannan Ranakun, kuma ya sadamu Da Falalar Da ya Tanadar Ga Masu Ibada A Wadannan Ranaku. Ameen Ya Allah.
✍Daga Dahiru Salihu*

Comments

Popular posts from this blog

KIMIYAR ALQUR'ANI DA ZAMANI A INA AKA HAƊU (1)

Kimiyyar Kur’ani Da Ta Zamani: A Ina Aka Hadu? (1) KIMIYYAR KUR'ANI DA ZAMANI By Baban Sadik Mun samu tambaya daga daya daga cikin masu karatu, wanda yake son sanin alakar dake tsakanin fahimtar malaman kimiyya na zamani kan abubuwan da suka shafi kimiyya, da kuma bayanin wasu abubuwa na kimiyya da Al-Kur’ani mai girma yayi. Shin, a ina suka hadu kuma a ina suka rabu? Wannan shi ne abin da zamu fara rubutu a kai daga wannan mako illa maa sha Allahu. A sha karatu lafiya. Tambaya “Abban Sadik, an ce masana Kimiyya na zamani sun tabbatar da wasu daga cikin Kimiyyar Al-Kur’ani mai girma. Wadanne ne daga ciki?” – Khaleel Nasir Kuriya, Kiru, Kano (GZG274): 07069191677 Gabatarwa Malam Khaleel Nasir muna godiya kwarai da wannan tambaya mai matukar muhimmanci, kuma Allah saka da alheri. Amsa wannan tambaya gaba dayanta na bukatar bincike na tsawon zamani mai dauke da hujjoji daga Kur’ani da kuma manyan littafan zamani. Domin harka ce da ta kumshi ilimi. Amma za mu yi iya kok...

Kimiyar Alqur'ani Da Zamani Part(2)

Kimiyyar Kur’ani Da Ta Zamani: A Ina Aka Hadu? (2) KIMIYYAKUR'ANI DA ZAMANI By Baban Sadik Wannan shi ne kashi na biyu cikin jerin kasidun da muke bincike na musamman kan alakar dake tsakanin kimiyyar Kur’ani da ta Zamani. A sha karatu lafiya. HALITTAR DUNIYA ——————————————— Binciken Kimiyyar Zamani Abu na farko da Malaman kimiyyar sararin samaniya (Astronomers ko Astrophysicists) suka binciko dangane da asalin duniya baki dayanta, ba wacce muke rayuwa cikinta ba kadai, shi ne asali a cure take wuri daya; komai a dunkule. Ma’ana asalin duniya wani curi ne na jiki mulmulalle, ko kuma Sadima, (kamar yadda Farfesa Muhammad Hambali Jinju ya kira shi) wato Primary Nebula kenan a Turance. Sai wannan curi ya fashe, ya kuma tarwatse, wato matakin Secondary Separation kenan. Hakan ya haifar da samuwar kura mai tattare da iska mai dimbin yawa, wato Gaseous Mass. Wannan tarwatsewar ce ta haifar da samuwar dukkan halittun da ke duniyar, daga wannan duniyar da muke ci...

KIMIYAR LANTARKI A SAUWAKE (1)

Kimiyar Lantarki A Sawwake (1) KIMIYYALANTARKI By Baban Sadik A yau za mu fara bincike na musamman kan abin da ya shafi kimiyyar lantarki da yadda makamashin lantarki ke samuwa, duk a mahangar kimiyya. Wannan shi ne kashi na daya mai dauke da mukaddima. A sha karatu lafiya. Mabudin Kunnuwa Bayan kwashe makonni sama da goma shabiyar muna amsa tambayoyi da yin bayani kan tsokacin masu karatu, a wannan mako dai na lura cewa idan muka ci gaba da amsa tambayoyi kadai, shafin na iya gudanuwa na tsawon lokaci ba tare da an tattauna wani abu ba; domin a duk mako tambayoyi na dada karuwa ne. Don haka naga dacewar dakatar da amsa tambayoyi. A yanzu sabon tsarinmu shi ne, za mu rika amsa tambayoyi ne bayan gama maudu’in da muka dauka; ko da kuwa zai kai mu makonni goma ne. Illa dai tabbacin da zan iya baiwa masu karatu shi ne, zan rika amsa tambayoyi ko bukatun masu neman kasida ko karin bayani na gaggawa ne ta Imel. Amma abin da ya shafi tsokaci, sai mun gama maudu’in da muka dauka ...