Skip to main content

Saƙon Wata ƙungiyar Yorubawa ga 'Makiyaya'

Labaran Siyasa
Ku gaggauta barin yankin mu ko mu yi 'fito na fito' da ku - Afenifere ta gargadi makiyaya ▷ Nigeria news | Legit.ng Ku gaggauta barin yankin mu ko mu yi 'fito na fito' da ku - Afenifere ta gargadi makiyaya
Naziru Dalha Taura

Afenifer, babbar kungiyar 'yan kabilar Yoruba, ta umarci Fulani Makiyaya da ke yankin kudu maso yamma da su gaggauta barin yankinsu ko kuma su fuskanci fushinsu, kamar yadda jaridar The Cable ta rawaito ranar Alhamis. Yayin wani taro da manema labarai da shugabannin kungiyar suka yi a Legas, Afenifere ta roki majalisun kasa da kar su canja dokar da zata bawa gwamnatin tarayya ikon karbar filaye daga gwamnatin jihohi domin yin tsarin Ruga. Da yake karanta jawabi amadadin sauran shugabannin kungiyar, Dattijo Ayo Adebanjo, ya ce ba zasu yarda kashe-kashen da ake yi a yankin ya cigaba ba.

Ragowar shugabannin kungiyar da suka halarci taron sun hada da Banji Akintoye, Femi Okunrounmu, Yinka Odumakin, Supo Shonibare da Sola Lawal. Adebanjo ya ce kungiyar Afenifere na bukatar Fulani makiyaya su gaggauta barin yankin kudu maso yamma ko kuma idan sun ki, jama'ar yamkin su yi 'fito na fito' da su.

Wani bangaren na jawabin kungiyar ya ce, "ba zamu yarda mutanen da suka ki yarda zababbun gwamnonin mu su kafa 'yan sandan jihohi ba yanzu kuma suke son karbar kasar mu domin yi wa makiyayan da suka hana mu zama lafiya wurin zama ba. "Mu na bukatar su gaggauta barin kasar 'yan kabilar Yoruba. Kuma idan suka ki yin hakan nan da dan wani lokaci, ba zamu hana mutanen mu yin 'fito na fito' da su ba."

Kungiyar ta kara da cewa ba zata yarda ta zuba ido ba a yayin da ake cigaba da zubar da jinin 'ya'yanta ba don kawai ana ikirarin zama a kasa daya mai bin tsarin tarayya ba. Kazalika, sun yi kira da a gaggauta koma wa tsarin mulki da ya bawa kowanne yanki damar cin gashin kansa.

nameMuhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu. Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta: Facebook: https://facebook.com/legitnghausa Twitter: https://twitter.com/legitnghausa Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng Source: Legit.ng

Tags: YorubaHausa NewsRikicin MakiyayaAbun MamakiAbun Bakin Ciki

Comments

Popular posts from this blog

KIMIYAR ALQUR'ANI DA ZAMANI A INA AKA HAƊU (1)

Kimiyyar Kur’ani Da Ta Zamani: A Ina Aka Hadu? (1) KIMIYYAR KUR'ANI DA ZAMANI By Baban Sadik Mun samu tambaya daga daya daga cikin masu karatu, wanda yake son sanin alakar dake tsakanin fahimtar malaman kimiyya na zamani kan abubuwan da suka shafi kimiyya, da kuma bayanin wasu abubuwa na kimiyya da Al-Kur’ani mai girma yayi. Shin, a ina suka hadu kuma a ina suka rabu? Wannan shi ne abin da zamu fara rubutu a kai daga wannan mako illa maa sha Allahu. A sha karatu lafiya. Tambaya “Abban Sadik, an ce masana Kimiyya na zamani sun tabbatar da wasu daga cikin Kimiyyar Al-Kur’ani mai girma. Wadanne ne daga ciki?” – Khaleel Nasir Kuriya, Kiru, Kano (GZG274): 07069191677 Gabatarwa Malam Khaleel Nasir muna godiya kwarai da wannan tambaya mai matukar muhimmanci, kuma Allah saka da alheri. Amsa wannan tambaya gaba dayanta na bukatar bincike na tsawon zamani mai dauke da hujjoji daga Kur’ani da kuma manyan littafan zamani. Domin harka ce da ta kumshi ilimi. Amma za mu yi iya kok...

UMMDATUL AHKAM: BABIN BAYANIN JININ HAILA

UMDATUL AHKAM باب الحيـــض: 40- عن عائشة رضي الله عنها "أَنَّ فَاطِمَةَ بِنْتَ أَبِي حُبَيْشٍ سألت النبي صلى الله عليه وسلم، فَقَالت: إِنِّي أُسْتَحَاضُ فَلاَ أَطْهُرُ، أَفَأَدَعُ الصَّلاَةَ؟ فقالَ: لاَ، إِنَّ ذَلِكَ دَمُ عِرْقٍ، وَلَكِنْ دَعِي الصَّلاَةَ قَدْرَ اْلأَيَّامِ الَّتِي كُنْتِ تَحِيضِينَ فِيهَا، ثُمَّ اغْتَسِلِي وَصَلَّى". وفي رواية: "وَلَيْسَتْ بِالْحَيْضَةِ، فَإِذَا أَقْبَلَتِ الْحَيْضَةُ فَاتْرُكِي الصَّلاَةَ فِيهَا، فَإِذَا ذَهَبَ قَدْرُهَا فَاغْسِلِي عَنْكِ الدَّمَ وَصَلِّي". BABUN DA ZAI YI BAYANI A GAME DA HUKUNCIN JININ HAILA: 40- An karvo daga (Nana) Aishatu (R.A) tace haqiqa Faximatu xiyar Abi Hubaishin ta tambayi annabin Allah (S.A.W.) sai tace (da shi): (Ya ma'aikin Allah) ni mace ce da nake yawan zubar jinin haila bani da tsarki shin ko na bar yin sallah? Sai ma'aiki (S.A.W.) yace da ita a'a, (ai ba kya bari ba) domin ai shi wannan wani jinin da yake zubowane daga wata jijiya (dake jikin mahaifa), sai dai ke abin da ya wajaba kiy...

Maganin Yawan Fitar Ruwa Mai Kai-kayj Afarjji

Ga Mata masu lalurar fitar ruwa masu Kaikayi daga Farjin su.  A gwada daya daga cikin wadannan:- 1)A samu Saiwar Garafuni da Sassaken Magarya, sai a tafasa, idan ya dan huce sai mace ta dinga kama ruwa da shi. Kullum sau daya. Yana maganin budewa da kaikayi. 2) A samu Garafuni da Sassaken Sanya sai a tafasa, mace ta dinga shan rabin kofi da safe, rabi da yamma. Yana fitar da dattin mara da maganin farin ruwa mai wari. . 3) A samu Furen Tumfafiya, sai a shanya ya bushe, a daka a dinga zubawa a cikin Nono ana sha. Yana magance matsalar ruwan infection. . 4) A samu Lalle da Ganyen Magarya da Kanumfari, a hada waje daya a daka sannan a tafasa a zuba farin miski a ciki. Idan ya dan huce sai ta shiga ciki ta zauna tsawon kamar minti goma. Yin haka yana maganin kaikayi da kuraje da budewa da dadewar gaba. 5) A samu Kabewa a dafa ta, bayan an dafa sai a tsame daga ruwa a jajjagata ko a birga, a zuba Madara ko Nono sannan a sa Zuma a sha. Wannan yana mganin rashin sha’awa da bushewa da rash...