HAUSA JAGORAN MAHAJJACI DA MAI UMARA Wallafar Ɗalal bn Ahmad al-‘Aqeel
GabatarwarMai Girma Shaikh Salih bn Abdul’Aziz bn Muhammad Aal-al-Shaikh
Shaikh Salih bn Abdul’Aziz bn Muhammad Aal-al-Shaikh[]Yabo da godiya su tabbata ga Allah wanda ya farlanta hajin Ɗakin Allah mai alfarma ga wax anda suke da iko daga cikin bayinSa, kuma Ya sanya aikin Haji kuvutacce ya zama kankarace ga zunubai da laifuffuka.
Salatin Allah da amincinSa su tabbata ga za- vavven Annabi, fiyayyen wanda yayi Ɗawafi da sa’ayi, kuma mafi girman wanda yayi talbiya kuma yayi addu’a. Wannan salati da aminci su tabbata har ga iyalan gidansa da sahabbansa da wanda ya bishi da kyautatawa kuma yayi koyi dashi.
Bayan haka, ya xan uwana Alhaji mai daraja, ina maka maraba da lale zuwa wannan qasa mai aminci, kuma ina roqon Allah – Tsarki ya tabbata a gar- eShi - ya sauqaqe maka gudanar da ibadarka ta aikin haji da umara ta fuskar da Allah zai yarda da ita, kuma Allah ya sanya aikin ya zama da ikhlasi domin Allah sannan ya zama bisa koyarwar AnnabinSa – sallallahu alaihi wa sallam.
Kuma ina roqon Allah ya karvi aikin sannan ya sanyashi cikin ma’aunin aikinka.
Ya ɗan uwana mahajjaci, idan kowace tawagar matafiya suna da shugaba, kuma kowane ayari yana da jagora mai nuna masa hanya, to lallai shugaban ayarin mahajjata shine Muhammadu – sallallahu alaihi wa sallam.
Kuma jagorar wannan ayari ita ce hanyarsa da sunnarsa. Domin kuwa shine mai cewa: “Ku riqi ibadar hajinku daga gareni”.
Domin haka ne ya zama dole ga duk mai nufin Ɗakin Allah domin Haji ko Umara ya koyi tsarin Annabi da kuma tafarkinsa – sallallahu alaihi wa sal- lam - ta hanyar amintattun littattafan koyarda ibadar Haji, da kuma tambayar malamai bisa duk abinda ya shige masa duhu.
To ya kai alhaji, ga wannan littafi gabanka wanda kalmominsa a bayyane suke, ya fito cikin sabon sunfuri, zai sauqaqa maka fahimtar hukunce huku- ncen haji da Umara da salon bayani quru-quru, tare da hotuna masu fito da komai filla-filla. Ina fata zaka xaukeshi a matsayin jagoranka a hajinka da umararka.
Lallai Ma’aikatar Al-amurran Musulunci ta Saudi Arabia tana murna da wannan matsayi da Allah ya bata na yi maka hidima ta baya- nin duk abinda zaka bukaceshi idan wani abu ya shige maka duhu, domin kuwa, ta tattali wasu cibiyoyi da rumfuna na musamman da 5 Mai Girma
*Salih bn Abdul’Aziz Aal al-Shaikh zaka samu malaman da zasu nuna maka hanya, domin aiki da faxin Allah Ta’ala “Ku tambayi ma’abuta Ambato (ilimi) in ba ku sani ba”.
* A qarshen wannan shimfixa tawa, ba zan qarqareta ba sai na yi godiya mai tarin yawa ga xan uwana Shaikh Xalal bn Ahmad al-Aqeel wanda ya wal- lafa wannan littafin jagora. Kuma ina roqon Allah ya sanya wannan littafi da kuma dukkan wani kokari da gudumowa da wannan bawan Allah ya ke yi a wannan fage, ya sanyata cikin ma’aunan kyawawan ayyukansa, kuma ya kambama masa sakamakonsa da shi da abo- * kan aikinsa na kwamitin rabawa alhazai da masu umara littattafai da rubuce- rubucen addini da ke Jiddah, bisa wannan aiki mai albarka. Idan da wata wasiyya da zanyi maka ya baqon Xakin Allah, to zan maka wa- siyya tare ni kaina cewa ka ribaci wannan lokaci mai daraja wajen duk wani aiki da zai jawo yardar Allah wanda kazo a matsayin baqonSa, kuma ka sauka cikin iyakokin XakinSa, tare da barin duk abinda zai jawo fushinSa kuma ya ke qi. * Allah – Ta’ala – yana cewa:
Comments
Post a Comment