Skip to main content

UMMDATUL AHKAM: BABIN BAYANIN JININ HAILA

UMDATUL AHKAM
باب الحيـــض:
40- عن عائشة رضي الله عنها "أَنَّ فَاطِمَةَ بِنْتَ أَبِي حُبَيْشٍ سألت النبي صلى الله عليه وسلم، فَقَالت: إِنِّي أُسْتَحَاضُ فَلاَ أَطْهُرُ، أَفَأَدَعُ الصَّلاَةَ؟ فقالَ: لاَ، إِنَّ ذَلِكَ دَمُ عِرْقٍ، وَلَكِنْ دَعِي الصَّلاَةَ قَدْرَ اْلأَيَّامِ الَّتِي كُنْتِ تَحِيضِينَ فِيهَا، ثُمَّ اغْتَسِلِي وَصَلَّى".
وفي رواية: "وَلَيْسَتْ بِالْحَيْضَةِ، فَإِذَا أَقْبَلَتِ الْحَيْضَةُ فَاتْرُكِي الصَّلاَةَ فِيهَا، فَإِذَا ذَهَبَ قَدْرُهَا فَاغْسِلِي عَنْكِ الدَّمَ وَصَلِّي".

BABUN DA ZAI YI BAYANI A GAME DA HUKUNCIN JININ HAILA:
40- An karvo daga (Nana) Aishatu (R.A) tace haqiqa Faximatu xiyar Abi Hubaishin ta tambayi annabin Allah (S.A.W.) sai tace (da shi): (Ya ma'aikin Allah) ni mace ce da nake yawan zubar jinin haila bani da tsarki shin ko na bar yin sallah? Sai ma'aiki (S.A.W.) yace da ita a'a, (ai ba kya bari ba) domin ai shi wannan wani jinin da yake zubowane daga wata jijiya (dake jikin mahaifa), sai dai ke abin da ya wajaba kiyi shine ki bar yin sallah gwargwadon kwanakin da kikeyin hailarki a ciki, sannan kuma sai ki yi wanka ki ci gaba da yin sallarki.
Amma a cikin wata ruwayar kuma cewa yayi (ai shi wannan jini ba jinin haila bane). Ke dai idan hailarki ta zo sai ki bar yin sallah a cikinta idan kuma gwargwadon yadda kike yin ta ya wuce sai kiyi wanka ki ci gaba da yin sallah.

 

 
41-وعن عائشة رضي الله عنها "أَنَّ أُمَّ حَبِيبَةَ اسْتُحَيْضَتْ سَبْعَ سِنِينَ، فَسَأَلَتْ رَسُولَ الله صلى الله عليه وسلم عَنْ ذَلِكَ؟ فَأَمَرَهَا أَنْ تَغْتَسِلَ، فَكَانَتْ تَغْتَسِلُ لِكُلِّ صَلاَةٍ".
41-An karvo daga Nana Aisha (R.A) tace Ummu Habibata ta kasance ta yi jinin istahala har na tsawon shekara bakwai (daganan) sai ta tambayi ma'aikin Allah (S.A.W.) akan haka? Sai shi kuma ya umarce ta da yin wanka sai ya zamo ta kasance tana yin wanka ga kowacce sallah (wato bata haxa sallah biyar da alwala xaya).

 
42-وعن عائشة رضي الله عنها قالت: "كُنْتُ أَغْتَسِلَ أَنَا ورسولُ الله صلى الله عليه وسلم مِنْ إِنَاءٍ وَاحِدٍ كَلاَنَا جُنُبٌ. وَكَانَ يَأْمُرُنِي فَأَتَّزِرُ، فَيُبَاشِرُنِي وَأَنَا حَائِضٌ.وَكَانَ يَخْرِجُ رَأْسَهُ إِلَيَّ وَهُوَ مُعْتَكِفٌ، فَأَغْسلُهُ وَأَنَا حَائِضٌ".
42-An karvo daga Nana Aishatu (R.A) tace ni na kasance ina yin wanka ni da ma'aikin Allah (S.A.W.) a cikin qwarya xaya, kowanne xayanmu yana da janaba, sannan ya kasance yana umartata sai in xaura zani shi kuma sai ya rungumeni alhali ina haila. Hakanan kuma ya kasance yakan turo min kansa a yayin da yake ittikafi (a masallaci) sai ni kuma in wanke masa alhali ina haila.
43-وعن عائشة رضي الله عنها قالت: "كان رسول الله صلى الله عليه وسلم يَتَّكِئُ فِي حِجْرِي وَأَنَا حَائِضٌ، فَيَقْرَأُ الْقُرْآنَ"
43-An karvo daga Nana Aishatu (R.A) tace manzon Allah (S.A.W.) ya kasance yana kashingixa akan cinyata alhali ina haila yakan kuma karanta alqur'ani yana kuma kashingixan akan cinyar tawa.
44- وعن مُعاذة قالت: "سألت عائشة رضي الله عنها فقلت: مَا بَالُ الْحَائِضِ تَقْضِي الصَوْمَ وَلاَ تَقْضِي الصَّلاَةَ؟ فقالت: أحَرُورِيَّةٌ أَنْتِ؟ فَقلت: لَسْتُ بِحَرُورِيَّة، وَلَكِنِّي أَسْأَلُ، فقالت كان يُصِيبُنَا ذَلِكِ، فَنُؤْمَرُ بِقَضَاءِ الصَّوْمِ وَلاَ تُؤْمَرُ بِقَضَاءِ الصَّلاَةِ".
44-An karvo daga Ma'azata (R.A) tace (wata rana) na tambayi (Nana) Asihatu (R.A) sai nace da ita wai shin mai yasa ne mai jinin haila zata rama azumi ba zata rama sallah ba? Sai kuwa Nana Aisha tace (da ita) au ko kema kina daga cikin masu aqidar Haruriyyanci ne? (wato Khawarijawa) sai ita kuma tace a'a, a'a, ko kaxan ni ba mai bin aqidar Haruriyyanci ba ce, sai dai kawai ni ina tambayane kawai (Daga nan sai ita Nana Aishar) tace mun kasance irin wannan xin yana samun mu sai kawai a umarcemu da mu rama Azumi amma ba'a umatarmu da rama sallah.

Comments

Popular posts from this blog

KIMIYAR ALQUR'ANI DA ZAMANI A INA AKA HAƊU (1)

Kimiyyar Kur’ani Da Ta Zamani: A Ina Aka Hadu? (1) KIMIYYAR KUR'ANI DA ZAMANI By Baban Sadik Mun samu tambaya daga daya daga cikin masu karatu, wanda yake son sanin alakar dake tsakanin fahimtar malaman kimiyya na zamani kan abubuwan da suka shafi kimiyya, da kuma bayanin wasu abubuwa na kimiyya da Al-Kur’ani mai girma yayi. Shin, a ina suka hadu kuma a ina suka rabu? Wannan shi ne abin da zamu fara rubutu a kai daga wannan mako illa maa sha Allahu. A sha karatu lafiya. Tambaya “Abban Sadik, an ce masana Kimiyya na zamani sun tabbatar da wasu daga cikin Kimiyyar Al-Kur’ani mai girma. Wadanne ne daga ciki?” – Khaleel Nasir Kuriya, Kiru, Kano (GZG274): 07069191677 Gabatarwa Malam Khaleel Nasir muna godiya kwarai da wannan tambaya mai matukar muhimmanci, kuma Allah saka da alheri. Amsa wannan tambaya gaba dayanta na bukatar bincike na tsawon zamani mai dauke da hujjoji daga Kur’ani da kuma manyan littafan zamani. Domin harka ce da ta kumshi ilimi. Amma za mu yi iya kok...

Kimiyar Alqur'ani Da Zamani Part(2)

Kimiyyar Kur’ani Da Ta Zamani: A Ina Aka Hadu? (2) KIMIYYAKUR'ANI DA ZAMANI By Baban Sadik Wannan shi ne kashi na biyu cikin jerin kasidun da muke bincike na musamman kan alakar dake tsakanin kimiyyar Kur’ani da ta Zamani. A sha karatu lafiya. HALITTAR DUNIYA ——————————————— Binciken Kimiyyar Zamani Abu na farko da Malaman kimiyyar sararin samaniya (Astronomers ko Astrophysicists) suka binciko dangane da asalin duniya baki dayanta, ba wacce muke rayuwa cikinta ba kadai, shi ne asali a cure take wuri daya; komai a dunkule. Ma’ana asalin duniya wani curi ne na jiki mulmulalle, ko kuma Sadima, (kamar yadda Farfesa Muhammad Hambali Jinju ya kira shi) wato Primary Nebula kenan a Turance. Sai wannan curi ya fashe, ya kuma tarwatse, wato matakin Secondary Separation kenan. Hakan ya haifar da samuwar kura mai tattare da iska mai dimbin yawa, wato Gaseous Mass. Wannan tarwatsewar ce ta haifar da samuwar dukkan halittun da ke duniyar, daga wannan duniyar da muke ci...

KIMIYAR LANTARKI A SAUWAKE (1)

Kimiyar Lantarki A Sawwake (1) KIMIYYALANTARKI By Baban Sadik A yau za mu fara bincike na musamman kan abin da ya shafi kimiyyar lantarki da yadda makamashin lantarki ke samuwa, duk a mahangar kimiyya. Wannan shi ne kashi na daya mai dauke da mukaddima. A sha karatu lafiya. Mabudin Kunnuwa Bayan kwashe makonni sama da goma shabiyar muna amsa tambayoyi da yin bayani kan tsokacin masu karatu, a wannan mako dai na lura cewa idan muka ci gaba da amsa tambayoyi kadai, shafin na iya gudanuwa na tsawon lokaci ba tare da an tattauna wani abu ba; domin a duk mako tambayoyi na dada karuwa ne. Don haka naga dacewar dakatar da amsa tambayoyi. A yanzu sabon tsarinmu shi ne, za mu rika amsa tambayoyi ne bayan gama maudu’in da muka dauka; ko da kuwa zai kai mu makonni goma ne. Illa dai tabbacin da zan iya baiwa masu karatu shi ne, zan rika amsa tambayoyi ko bukatun masu neman kasida ko karin bayani na gaggawa ne ta Imel. Amma abin da ya shafi tsokaci, sai mun gama maudu’in da muka dauka ...